Rahotanni na cewa jami’an kungiyar ‘yan tawaye da na Gwamnati a jumhuriyar Afirka ta tsakiya sun kai ga cimma daidaituwar kafa Gwamnatin hadin gwiwar da zata kasance karkashin jagorancin shugaba Francois Bozize.
Wakiliyar MDD a zauren tattaunawar neman zaman lafiya Margaret Vogt, tayi bayanin dalla-dallar yadda aka kai ga cimma daidaituwar ta jiya Juma’a bayan da wakilan sassan biyu suka zauna suka tattauna domin fahimtar juna a Libreville, babban birnin kasar Gabon.Kwamatin sulhu da tsaro na MDD yay aba da cimma daisdaituwar a Rikicin jumhuriyar Afirka ta tsakiya.
Wakiliyar MDD a zauren tattaunawar neman zaman lafiya Margaret Vogt, tayi bayanin dalla-dallar yadda aka kai ga cimma daidaituwar ta jiya Juma’a bayan da wakilan sassan biyu suka zauna suka tattauna domin fahimtar juna a Libreville, babban birnin kasar Gabon.Kwamatin sulhu da tsaro na MDD yay aba da cimma daisdaituwar a Rikicin jumhuriyar Afirka ta tsakiya.