Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Bata Cimma Yarjejeniya Ba Da Iran Akan Nukiliya


Hoton Herman Nackaerts kennan, na Hukumar Makamashin Nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya. Junairu 15, 2013.
Hoton Herman Nackaerts kennan, na Hukumar Makamashin Nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya. Junairu 15, 2013.
Shugaban spetocin Hukumar Makamashin Nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce ba’a cimma wata yarjejeniya da kasar Iran akan binciken shirin nukiliyarta wanda ya jawo cece kuce ba. Amma yace, a watan gobe idan Allah ya kaimu za a yi wani taro akan wannan batu.

Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ko kuma IAEA a takaice, Herman Nackaerts ya fada a yau Jumma’a cewa, shi da tawagarsa sun isa filin saukar jiragen Vienna bayan ganawar kwanaki biyu a Tehran babban birnin kasar Iran.

Yayin da yake bayyana bambamcin dake tsakaninsu da kasar Iran din, Nackaerts ya ce bangarorin biyu basu iya cimma matsaya daya ba kan yadda za’a warware matsalolin ba. Ya ce zasu sake tattaunawa ranar 12 ga watan gobe, idan Allah ya kaimu.

Hukumar ta IAEA ta yi zaton, samun sukunin shiga sansanin soja a Parchin, wurin da ke kasashen yammacin turai ke na da alaka da kera makaman nukiliya. Iran ta dage akan cewa wurin, sansani ne na soja kawai, kuma shirinta na nukiliya, tana yi ne a saboda bukatun samun zaman lafiya.
XS
SM
MD
LG