WASHINGTON, DC —
An kashe sojojin kasar Chadi uku yau Jumma'a, a lokacin da wani dan harin kunar bakin wake ya tayar da bam a cikin wata kasuwa a yankin arewacin Mali.
Shaidu da kuma 'yan sanda sun ce wannan dan kunar bakin wake ya auna sojojin ne a birnin Kidal dake arewacin Mali, ya kashe su da kuma kansa.
Wasu sojojin su hudu sun ji rauni tare da fararen hula da dama a wannan harin.
Wannan harin kunar bakin wake shi ne na uku irinsa a birnin Kidal, tun watan Janairu, lokacin da Faransa ta jagoranci wani farmakin da ya 'yantar da wannan birni tare da wasu da dama a arewacin kasar daga hannun tsagera 'yan kishin Islama.
Akwai sojojin Faransa su dubu 4 dake gwabzawa da tsageran. Sannan akwai sojojin Mali da na kasashen Afirka, ciki har da dubu 2 daga Chadi dake yakar tsageran.
Shaidu da kuma 'yan sanda sun ce wannan dan kunar bakin wake ya auna sojojin ne a birnin Kidal dake arewacin Mali, ya kashe su da kuma kansa.
Wasu sojojin su hudu sun ji rauni tare da fararen hula da dama a wannan harin.
Wannan harin kunar bakin wake shi ne na uku irinsa a birnin Kidal, tun watan Janairu, lokacin da Faransa ta jagoranci wani farmakin da ya 'yantar da wannan birni tare da wasu da dama a arewacin kasar daga hannun tsagera 'yan kishin Islama.
Akwai sojojin Faransa su dubu 4 dake gwabzawa da tsageran. Sannan akwai sojojin Mali da na kasashen Afirka, ciki har da dubu 2 daga Chadi dake yakar tsageran.