Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nijar Tana Farautar Fursunoni Masu Alaka Da Ta'addanci


Soojin Nijar tsaye a kofar babban gidan kurkukun Yamai, a bayan wani farmakin da ya janyo mutuwar mutane da dama, da kuma tserewar wasu fursunonin wadanda ake tsammanin su na da hannu a ayyukan ta'addanci.
Soojin Nijar tsaye a kofar babban gidan kurkukun Yamai, a bayan wani farmakin da ya janyo mutuwar mutane da dama, da kuma tserewar wasu fursunonin wadanda ake tsammanin su na da hannu a ayyukan ta'addanci.

Kwanaki biyar bayan farmakin da aka kai kan babban gidan kurkuku na birnin Yamai, gwamnatin Nijar ta fito da hotunan mutane 9 masu alaka da ta'addanci da suka tsere

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun fito da hotunan wasu mutane 9 da suka ce masu alaka da ayyukan ta'addanci ne, wadanda suka balle daga gidan kurkukun birnin Yamai a lokacin wani farmakin da ya kashe fursunoni 22 a ranar asabar da ta shige.

Wakilin Sashen Hausa, Abdoulaye Mamane Ahmadou, yace daga cikin mutanen 9 da ake nema ruwa a jallo, har da wani mutumi mai suna Chebani, wanda ya taba kashe Ba-Amurke daya da wasu larabawa 'yan kasar Saudi Arabiya su 4.

Mahukuntan Nijar, su na fata bayyana wadannan hotuna, zasu taimaka musu wajen ba jama'ar kasar damar sanya hannu a farautar wadannan mutane da ake yi.

Ga cikakken rahoton Abdoulaye daga birnin Yamai
Rahoto Daga Nijar Kan Mutanen Da Suka Gudu Daga Kurkuku, Ake Kuma Nemansu - 2:53
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:53 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG