Gwamnatin Najeriya zata biya wadanda rikicin zaben 2011 ya rutsa da su diyya. A karo na farko ta fitar da nera miliyan dubu goma sha biyar na biyan jihohi tara. Cikin jihohin har da ma jihar Bauchi inda wakilinmu ya samu ya zanta da wasu da abun ya shafa.
A cikin kudin da aka ware ma jihohi tara a kashin farko, jihar Bauchi zata samu nera miliyan dubu daya da miliyan dari bakwai. To sai dai babu wanda kason suka shigo hannunsa tukunna a jihar Bauchi. Wani Alhaji Auwalu Karfen Ningi ya ce shi da sauran mutane talatin da hudu da suka yi asarar dukiyoyinsu ko kwabo basu samu ba tukunna. Sun tattaka zuwa ofisoshin karamar hukuma da na jiha basu ci nasara ba. A jihar jami'an gwamnati sun ce su ma a kafar radiyo suka ji amma babu abun da ya shigo aljihun gwamnatin jihar game da biyan diyar.
Wakilinmu Abdulwahab Mohammed ya yi karin bayani a rahotonsa.
A cikin kudin da aka ware ma jihohi tara a kashin farko, jihar Bauchi zata samu nera miliyan dubu daya da miliyan dari bakwai. To sai dai babu wanda kason suka shigo hannunsa tukunna a jihar Bauchi. Wani Alhaji Auwalu Karfen Ningi ya ce shi da sauran mutane talatin da hudu da suka yi asarar dukiyoyinsu ko kwabo basu samu ba tukunna. Sun tattaka zuwa ofisoshin karamar hukuma da na jiha basu ci nasara ba. A jihar jami'an gwamnati sun ce su ma a kafar radiyo suka ji amma babu abun da ya shigo aljihun gwamnatin jihar game da biyan diyar.
Wakilinmu Abdulwahab Mohammed ya yi karin bayani a rahotonsa.