Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Neman Gudunmuwar Jini a Asibitocin Abuja


Mutane a inda Bom ya fashe a tashar motar Nyanya Abuja, Najeriya.
Mutane a inda Bom ya fashe a tashar motar Nyanya Abuja, Najeriya.

Bayan fashewar tagwayen boma-bomai a tashar motar Nyanya dake birnin tarayyar Abuja, hukumomi sunce an rasa rayuka sama da mutum 71, da kuma sama da 100 wadanda suka jikkata. Wasu da suka rayu na bukatar tallafin jinni, shiyasa likitocin asibitocin da aka kai masu jinya suke kira ga jama'a su bada tallafin jini.

Shugaban hukumar kawo dauki na gaggawa a babban birnin tarayya Abuja, Abbas Idris yayi kira ga jama’a da su gaggauta kawo gudunmuwar jini.

Mr. Abbas yace "neman wannan taimako yazama wajibi domin bukatar da ake dashi domin yiwa wadanda suka jikkata magani."

Kawo yanzu ana samun nasarar yiwa mutane da suka ji rauni magani yadda ya kamata, kuma suna samun sauki, a cewar jami'an asibitocin.

Abbas Idris ya kara da cewa "hukumar babban birnin taraiya Abuja ta dauki nauyin dawainiyar yiwa wadanda suka ji rauni magani.

Shugaban hukumar kawo daukin gaggawa, ya jaddada cewar likitocin dake kula da wadanda suka ji rauni sunce daga dukkan alamu mutanen zasu rayu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:13 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG