Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rundunar Hadin Gwiwar Kasashen Tafkin Chadi Sunyi Galaba


Rundunar ta bukaci jama’ar gari dasu taimaka wajen tona duk inda suka san cewa ‘yan Boko Haram suke labewa.

Rundunar hadin gwiwa na kasashen tafkin Chadi, tayi nasarar kashe wasu ‘yan Boko Haram tare da kwace wasu kayayyaki .

Kakakin rundunar hadin gwiwa na kasashen yakin tafkin Chadi, Kanal Muhammad Dole, yace wannan nasara na nuni da cewa hada karfi da akayi hakar tana cimma ruwa.

Yace yanzu an ci karfin ‘yan Boko Haram ganin cewa basu iya daukar bindiga da motoci kamar yadda suke yi a can baya suna kaddamar da hare hare.

Ya kara da cewa domin dorewar wannan nasara ya bukaci jama’ar gari dasu taimaka wajen tona duk inda suka san cewa ‘yan Boko Haram suke labewa.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:12 0:00

XS
SM
MD
LG