Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Trump Yace Shi Ne Zai Kawo Karshen Neman Zabe Yadda Yake So


Donald Trump
Donald Trump

Yayinda yake kara samun matsala bisa ga zargin kokarin yin lalata da wasu karin mata suka fito fili suna yi Trump sai kame kame ya keyi

Dan takarar shugaban kasa a jami’iyar Republican a nan Amurka Donald Trump ya lashi takobin kawo karshen yankin neman zabensa ta yadda yake so.

Trump ya nuna halin ko’unkula a kan yanda kososhin jami’iyar suke fita daga kwamitin kampensa, bayan da aka fitar da wani faifansa da aka dauka 2005, inda shi Trump din yake kalamai marsa kyau ga mata da kuma nuna Gadara da lalata dasu.

Yace yana cike da fushi da yan jami’iyarsu ta Republican, yana fadawa magoya bayansa a shekaranjiya Laraba a babban filin daga jihar Florida dake kudu maso gabashin kasar. Yace basu nuna goyon bayansu ga mutane.

XS
SM
MD
LG