Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

ISTA'ILA TANA KAFA SHINGE A YANKIN FALASDINAWA


Babbar Kotun kasar Isra’ila tace dolene gwomnatin kasar bude wata hanyar zage da za’a bi daga inda take gina katangar shinge kanta daga yankin yammacin kogin Jordan. A yau Alhamis ne kotun Kolin kasar ta yanke wannan hukunci kan wata kara da Palasdinawa dake zaune a wani kauye suka shigar dake cewa wannan shinge da Isra’ila ke kafawa a gefen garin Qalqilya na yankin Palasdinawa, ta toshe musu hanyarsu ta zuwa wasu yankunan yanmmacin kogin Jordan din. wani kwamiti mai alkalan Isra’ila 9 daya saurari wannan karar yace Isra’ila tana da ‘yancin gina katanga a yankinta domin kare al’umarta daga hareharen ‘yan kunan bakin wake. Bara ne kotun duniya ta yanke hukunci cewa wannan katanga da isra’ila take ginawa baya bisa ka’ida.

XS
SM
MD
LG