Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ma'aikatar Tsaron Britaniya Ta Kaddamar Da Bincike Game Da Cin Zarafin Fursunoni 'Yan Iraqi


Ma'aikatar tsaro ta Britaniya ta kaddamar da abinda ta kira binciken soja na gaggawa kan zargin cin zarafin fursunoni 'yan Iraqi da aka nuna a hotunan bidiyo.

Wata sanarwar ma'aikatar ta yi tur da dukkan ayyukan cin zarafi ko mutunci, ko nuna keta, ta kuma ce zata binciki zargin aikata su gadan-gadan.

Jiya lahadi gidajen telebijin na Britaniya sun nuna wadannan hotunan bidiyo a bayan da jaridar "News of The World" ta fito da su.

A cikin hotunan, an ga sojojin Britaniya su na dukar matasa 'yan Iraqi masu zanga-zanga da aka kama da kulakai, su na kuma kai musu bugu da kafa. Jaridar ta ce an dauki hotunan a kudancin Iraqi a cikin shekarar 2004.

Firayim minista Tony Blair na Britaniya ya fada jiya lahadi cewar za a binciki wannan lamari sosai. ya ce akasarin sojojin Britaniya dake Iraqi su na gudanar da gagarumin aiki na taimakawa Iraqi ta zamo kasa mai bin tafarkin dimokuradiyya.

XS
SM
MD
LG