Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Babban Jami'in Ayyukan Jinkai Na Majalisar Dinkin Duniya Ya Tsere Daga Sansanin 'Yan Gudun Hijirar Darfur


Babban jami'in ayyukan jinkia na Majalisar Dinkin Duniya ya tsere daga wani sansanin mutanen da suka rasa matsuguni a yankin Darfur mai fama da fitina, a bayan da 'yan zanga-zanga suka rikide suka koma masu tayar da fitina a sanadin wani sabani.

Ala tilas Jan Egeland da 'yan tawagarsa suka arce daga sansanin Kalma litinin din nan a lokacin da gungun masu zanga-zangar dake neman karin kariya daga sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD, suka kai farmaki a kan wani tafinta. An yada jita-jitar cewa shi wannan tafinta yana da alaka da kungiyar banga ta Janjaweed wadda aka dora wa alhakin akasarin tabargazar da aka aikata a yankin Darfur.

Egeland da ma'aikatan agaji sun koma Nyala, babban birnin lardin Darfur ta kudu. Daga baya, ya fadawa 'yan jarida cewar a bayan da tawagarsa ta bar sansanin, gungun jama'a sun kai farmaki a kan tashar 'yan sandan Kungiyar Tarayyar Afirka suka kashe wani tafinta.

Wannan ziyara ta Egeland ta biyo bayan yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla a tsakanin babbar kungiyar 'yan tawaye ta Darfur da gwamnatin Sudan. Wasu kungiyoyin 'yan tawayen biyu ba su yarda da wannan yarjejeniya ba.

XS
SM
MD
LG