Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Bush ya ce Kasashen Duniya zasu nemi kafawa Iran takunkumi...


Shugaba Bush na Amirka yace kasashen duniya zasu kafawa kasar Iran Takunkumin karya tattalin arziki idan ta ci gaba da inganta sinadaren uranium a matsayin wani bangare na shirin Nukiliyarta mai sarkakakiyar da ake jayayya da ita. A ranar litinin ne Mr. Bush ya yi wannan kalamin a fadarsa ta White House a bayan da ya kare ganawa da firayi ministan Isra’ila Ehud Olmert, Mr. Bush ya ce idan kasar Iran tana da makaman Nukiliya a hannunta, zata iya zama barazana ga zaman lafiya a yankin.

Shugaban na Amirka yaki a zauna ido da ido ya tattauna da shugaban Iran din yana mai cewa Amirka a shirye take tayi magana da iran amma bisa sharadi in ta dakatar da wannan aiki nata, Kamar yada kwamitin sulhu na MDD ya bukaci tayi.

Firayi ministan Isra’ilan yace a yana goyon bayan kokarin Amirka na neman a kafawa kasar Iran Takunkumi. Shi kuwa shugaban kasar partisan Mahmoud Ahmadin Nejad jiya Litinin ya sake nanata barazanar da yayi can kwanaki akan isra’ila cewa yakamata a share kasar daga taswirar duniya baki daya.

Ya ce Isra’ila zata bace nan bada jimawaba. A lokaci da ake hira da shi a gidan Talbijin na NBC Firayiministan Isra’ila ya ce kasarsa ba zata amincewa kasar Iran ta mallaki Nukiliya ba. Sai dai ya ki fadan ko kasarsa zata kaiwa Parisa farmakin ba-zata nan gaba.

XS
SM
MD
LG