Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani Kakakin Gwamnatin Nijeriya Ya Ce An Sako 'Yan Koriya Ta Kudu Da Aka Sace


An sako 'yan kasar Koriya ta Kudu su tara da wani dan Nijeriya daya wadanda 'yan bindiga suka sace ranar laraba a yankin kudancin kasar.

Wani kakakin gwamnatin Jihar Bayelsa ya ce a yau jumma'a aka sako mutanen su goma ba tare da ko kwarzane ba. Dukkansu ma'aikatan kamfanin Daewoo na kasar Koriya ta Kudu ne, wanda yake gudanar da wani aikin bututu a Bayelsa.

Kakakin jihar ya ce an mika mutanen ga kamfanin da suke yi wa aiki. Ya ce ba a biya diyya domin sako su ba.

Ranar laraba da asubahi ne 'yan bindiga suka sace mutanen a garin Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.

Hare-hare da sace-sacen mutane sun zamo ruwan dare a yankin Niger Delta mai arzikin man fetur a Nijeriya. Kungiyoyin 'yan ta kife a yankin su na matsawa gwamnati lamba a kan ta bai wa al'ummar yankin karin kaso na arzikin mai.

XS
SM
MD
LG