<!-- IMAGE -->
A makon gobe ne ake sa ran Mukaddashin Shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan, zai nada sababbin Ministocisa da za su maye wadanda ya sauke ranar Laraba.
Wasu kafofi a Fadar Shugaban Kasa sun ce da alamar Mr Jonathan zai maida fiye da rabin Ministocin da ya sauke.
Mukaddashin Shugaban na Nijeriya, ya sauke daukacin Ministoci 42 din ne; a wani al’amari mai kama da yunkurin karfafa ikonsa a gwamnati.