Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Lebanon Tace ta Kama 'Yan Leken Asirin Isra'ila - 2002-02-26


Rundunar sojojin kasar Lebanon tace dakarunta sun kame mutane uku da ake zargin suna yiwa Isra'ila ayyukan leken asiri.

A yau Talata ne rundunar sojojin ta bada sanarwar cewa an kame mutanen ne bayan wani binciken da aka gudanar, wanda ya fallasa aika-aikar gungun masu aikin leken asirin, da kokarinsu na bayarwa da Isra‘ila wasu muhimman bayanai kan tsarin ayyukan sojojin Lebanon da Syria da kuma wasu bayanai a kan yadda Hizbullah ke gudanar da ayyukanta.

Mutanen da ake zargi da laifin leken asirin sun yi kokarin bai wa Isra'ila bayanan ayyukan cibiyoyin hada-hadar kudaden Lebanon. Amma bayanin da rundunar sojojin ta Lebanon ta hayar bai bayyana lokaci da wurin da aka kame mutanen ba, kazalika ba'a san jinsun da suka fito ba.

XS
SM
MD
LG