Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

MDD Ta Shawarci Kwango-Kinshasa Da Ta Girka Sojoji A Bakin Iyakarta... - 2002-05-03


Wata tawagar Kwamitin Sulhun MDD da take ziyarar nahiyar Afirka a yanzu, ta gabatar ad shawarar cewa ya kamata kasar Kwango-Kinshasa ta girka sojoji a bakin iyakarta, domin kare kasashe makwabtanta daga hare-haren 'yan tawayen dake buya cikin Kwangon.

Shugaban wannan tawaga ta MDD, jakada Jean-David Levitt na Faransa, shine ya bada wannan shawara a lokacin da suka ziyarci kasar Angola a jiya alhamis.

Shawarar tayi kiran da a girka rundunar hadin guiwa ta Rwanda da Kwango a kusa da bakin iyakar ita Kwangon da Rwanda. Har ila yau, sojojin Kwango Kinshasa zasu yi aiki tare da takwarorinsu na Uganda da Burundi wajen kafa rundunonin hadin guiwa a iyakokinsu.

Rwanda da Kwango-Kinshasa sun yi marhabin da wannan shawara.

Hare-hare daga tsallaken iyaka da 'yan tawayen Rwanda da Burundi da kuma Uganda suke kaiwa cikin kasashensu daga Kwango, na daya daga cikin musabbabin yakin basasar kasar Kwango Kinshasa.

XS
SM
MD
LG