Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

MDD Ta Kara Wa'adin Aikin Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya A Birnin Kabul - 2002-05-24


Ba tare da wata hamayya ba, Kwamitin Sulhun MDD ya jefa kuri'ar kara watanni shida a wa'adin aikin sojojin kiyaye zaman lafiya dake birnin Kabul a kasar Afghanistan.

Amma kuma Kwamitin ya ki yarda da kiran da shugaban gwamnatin rikon kwarya Hamid Karzai yayi, na a fadada ayyukan sojojin kiyaye zaman lafiyar zuwa wasu biranen na kasar Afghanistan.

Amurka ce ta gabatar da kudurin kara wa'adin aikin sojojin kiyaye zaman lafiyar su dubu 4 da 600. A ranar 20 ga watan Yuni ne wa'adin watanni shidan farko na rundunar zai kare.

A halin da ake ciki, hukumomin Afghanistan sun sako fursunoni 'yan Taleban su fiye da 500 daga wani gidan kurkukun da ya cika makil a yankin arewacin kasar. Ana tura fursunonin zuwa birnin Kabul a cikin motocin safa.

Wani kakakin ma'aikatar tsaron Amurka, ya shaidawa Muryar Amurka cewa jami'an sojan Amurka ba su da wata damuwa game da sako wadannan fursunoni da aka yi.

XS
SM
MD
LG