Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Turawa Manoma Akalla Biyar Zasu Gurfana Gaban Kotu Jumma'a A Zimbabwe - 2002-08-15


An umurci turawa manoma su akalla biyar a kasar Zimbabwe da su bayyana a gaban kotu gobe Jumma'a, a saboda sun ki bin umurnin gwamnati na ficewa daga cikin gonakinsu.

Sune na farko da zasu gurfana a gaban kotu, daga cikin dubban turawa manoman kasuwanci da suka ki bin umurnin gwamnati na ficewa daga cikin gonakinsu, domin a rarraba wadannan gonaki ga bakar fatan da ba su mallaki filayen noma ba, a karkashin shirin gwamnati na sake rarraba filayen kasar.

Lauyoyin da suke wakiltar manoman sun ce zasu kalubalanci wannan umurnin a saboda su a ganinsu ya sabawa tsarin mulki.

Idan aka samu manoman da laifi, ana iya yanke musu tara, ko kuma a daure su a gidan kurkuku na tsawon shekaru biyu.

A ranar laraba, wasu bakaken fata 'yan kama wuri zauna, sun fara tilasta yin aiki da umurnin ficewa daga cikin gonakin, inda suka fatattaki wani manomi da iyalansa daga cikin gonarsu.

XS
SM
MD
LG