Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Khatami Ya Ja Kunnen Amurka Game Da Kai Harin Soja Kan Iran - 2002-08-28


Shugaba Mohammed Khatami na kasar Iran ya ja kunnen Amurka game da kai wa kasarsa harin soja, yana mai cewa yin haka zai haddasa rashin kwanciyar hankali a fadin yankin Gabas ta Tsakiya.

Malam Khatami ya ce Iran zata yi bakin kokarinta domin kawar da duk wani abinda za a iya yin amfani da shi a zaman hujjar neman cin zalin kasarsa a fagen soja. Amma kuma ya lashi takobin cewa Iran zata kare 'yancinta da kuma muradunta idan har aka kai mata hari.

A lokacin da yake ganawa da 'yan jarida yau laraba a birnin Teheran, shugaba Khatami yayi kiran da a samu abinda ya kira "manufofi managarta" daga Amurka. Ya ce irin akidar da gwamnatin shugaba Bush ta runguma a yanzu, ta tsageranci ce, kuma zata iya nakkasa muradun Amurka.

Har ila yau ya sake jaddada adawarsa da kai harin soja a kan Iraqi, yana mai kashedin cewa yin haka zai yamutsa al'amuran tsaron duniya baki daya.

XS
SM
MD
LG