Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jami'an Afirka ta Yamma Suna Kokarin Shirya Tsagaita Wuta A Yakin Liberiya - 2003-06-10


Jami'an shiga tsakani na Afirka ta Yamma suna fatar yin tattaki zuwa Liberiya a yau talata domin suyi kokarin kulla shirin tsagaita wuta a tsakanin sojojin gwamnati da 'yan tawayen dake neman shugaba Charles Taylor yayi murabus.

A jiya litinin, jami'an kungiyar ECOWAS, wadda ke shiga tsakani a tattaunawar neman zaman lafiyar da ake yi a Ghana, sun tashi domin yin tattakin da zai hada da kasashen Guinea da Saliyo.

A yau talata suke shirin tattaunawa da shugaba Charles Taylor a Monrovia, babban birnin kasar.

Tun da fari, Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya, MDD, yayi kiran da a kawo karshen fadan da ake yi nan take a Liberiya. Wannan kira na MDD ya zo 'yan sa'o'i kadan a bayan da sojojin Faransa suka yi amfani da jiragen helkwaftoci masu saukar ungulu domin kwashe 'yan kasashen waje su fiye da 500, a yayin da sojojin 'yan tawaye suka doshi Monrovia.

A ranar lahadi, babbar kungiyar 'yan tawaye ta Liberiya, L.U.R.D., ta bai wa shugaba Taylor wa'adin kwanaki uku da ya sauka ko kuma zasu kai farmakin kwace babban birnin kasar.

XS
SM
MD
LG