Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kammala Taron Kolin Shugabannin Afirka Ta Yamma Kan Rikicin Ivory Coast - 2003-11-12


Shugabannin wasu kasashe bakwai na Afirka ta Yamma sun roki Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya, MDD, da ya duba yiwuwar kara karfin rundunar kiyaye zaman lafiyar majalisar a kasar Ivory Coast.

A cikin sanarwar da suka bayar a karshen taron kolin wuni guda da suka gudanar jiya talata a Accra, babban birnin kasar Ghana, shugabannin sun ce ana bukatar wannan runduna domin karfafawa, daga baya kuma domin maye gurbin wata runduna ta sojojin yankin dake kasar ta Ivory Coast a yanzu haka.

Har yanzu kasar Ivory Coast tana rabe, watanni hudu a bayan da aka cimma yarjejeniyar kawo karshen yakin basasar watanni 10, wanda ya barke a sanadin tawayen da bangaren arewacin kasar yayi.

Kungiyar ECOWAS, wadda ta dauki alhakin taron na Ghana, tana da sojoji kimanin dubu 1 da 500 a Ivory Coast, a bayan sojojin Faransa su dubu 4 wadanda ke lura da bakin iyakar da aka shata a tsakanin sassan masu yakar juna.

A jiya talata, babban sakataren MDD, Kofi Annan, yayi gargadin cewa idan ba a gaggauta sake hade kasar ba, zaben da aka shirya gudanarwa a shekarar 2005 ba zai yiwu ba.

A bayan shugaba John Kuffour na Ghana da shugaba Laurent Gbagbo na Ivory Coast, taron ya samu halartar shugabannin kasashen Togo, Nijar, Burkina Fasso, Nijeriya da kuma Benin.

XS
SM
MD
LG