Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Al Bashir Na Sudan Ya Ziyarci Masar


Shugaba Umar Hassan Al Bashir na Sudan, ya kai ziyara kasar Masar, a wani abu da ake wa kallon bijirewa sammacin da kotun kasa da kasa mai hukunta laifuffukan yaki ta ta bayar na a kamo mata shi ne.

Shugaba Hosni Mubarak shine ya taryi Mr. Bashir a filin Jirgin saman birnin Alkahira, daga nan kuma suka zarce kai tsaye da tattaunawar da jami'an kasashen biyu suka ce ta karkata ga wancan sammaci na kamo shugaban na Sudan.

Kotun ta kasa da kasa ta bukaci kasashen duniya da su taimaka a kamo mata Shugaba Al Bashir, amma babu alamun cewa Masar zata amsa wannan kira.

Ministan Harkokin Wajen Masar, Ahmad Aboul Gheti, ya fada a jiya Laraba cewa Masar bata amince da yadda kotun ke muzanta Al Bashir ba.

Masar dai tana daga cikin kasashen da basu sanya hannu a yarjejeniyar kafa kotun ba.

XS
SM
MD
LG