Har yanzu dai ba a kaiga cimma yarjejeniyar karshe ba a kan lamarin, amma dai a jiwo shugabannin kasashen turai suna yaba yarjejeniyar a matsayin wani gagarumin ci gaba.
Ministocin Raya Kasa na Kungiyar Tariyar Turai da suka fara wani taro a birnin Brussels a jiya Talata, sun tabbatar da cewar Hukumar Taraiyar Turai ta yanke shawarar haraje-haraje kan kayan da suka fito daga kasashen 80.
Ministan raya kasa na Jamus, Heidemarie Wiezorek-Zeul, wanda ya shugabanci taron takwarorin nasa, yace wannan shawara zata taimakawa al’amuran raya kasa.