Laraban nan wani babban jami’in Majalisar Dinkin Duniya ya fara ziyarar kwanaki hudu a Nigeria da jamhuriyar Niger, domin nazarin ambaliyar ruwar data yiwa tsakiya da kuma yammacin Afrika barna.
Ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi ta tapkawa tasa koguna a jamhuriyar Niger da wasu koguna cika suna batsewa, al’amarin da ya shafi kusan mutane miliyan daya da rabi, ya kashe akalla mutane dari uku da saba’in da bakwai.
Haka kuma ambaliyar ruwa tasa an sami bullar annobar ciwon kwalera a Nigeria da Niger, harma sakatariyar harkokin jin kai, Valerie Amos zata gana da kungiyoyin agaji taga yadda suke tinkarar wannan matsala. Kasashen Chadi da arewacin kasar Kamuru suma suna fama da matsalar bullar annobar kwalera.
Tuni kungiyar UNICEF da wasu kungiyoyin kasa da kasa suna agazawa Chadi. A farkon wannan wata na Okotoba nan Chadi ta bada rahoton cewa mutane dubu biyu da dari shidda ne suka kamu da kwalera a kasar,cutar ta kashe mutane dari da goma sha biyu.
Jjamuhuriyar Benin ce tafi fama da ambaliyar ruwar data kashe mutane arba’in da biyu. Gwamnmantin Benin tana taimakon kasashen duniya bayan data ayyana kasar a zaman yankin da bala’in ta yi wa barna matuka. Larabar ce , ake sa ran tawagar wakilan Majalisar Dinkin Duniya mai nazarin bala’i zata isa jamhuriyar Benin.