Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Alhazan Najeriya Sun Mika Koke Da Korafe-Korafe


Alhazan Najeriya sun koka cewa an ajiye su da nisa a Mina, a tazarar tafiyar kilomita 4 da kafa zuwa wurin jifan shedan
Alhazan Najeriya sun koka cewa an ajiye su da nisa a Mina, a tazarar tafiyar kilomita 4 da kafa zuwa wurin jifan shedan

Amirul Hajj, Mai martaba Shehun Borno, Alhaji Abubakar Umar Ibn el-Kanemi, alhazan na Najeriya suka mikawa korafe-korafen

Shugaban tawagar gwamnatin tarayyar Najeriya a aikin Hajjin bana, mai martaba Shehun Borno, Alhaji Abubakar Umar Ibn el-Kanemi ya ce ya samu korafe-korafe da dama daga alhazan Najeriya a lokacin da ya ziyarci masaukan su a Makka. A taron manema labaran da mai martaba Shehun Bornon ya kira a birnin Jeddah, ya fada cewa korafe-korafen suna da matukar mahimmanci kuma za su sanya su a cikin rahoton da za su mikawa gwamnatin Najeriya idan sun koma gida. Wakilin Sashen Hausa Mustapha Nasiru Batsari na cikin manema labaran da Shehun Borno ya yiwa bayani a birnin Jeddah:

Koke da korafin da alhazan Najeriya suka mikawa amirul Hajj - 2:06
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:06 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG