Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Allassane Quattara ya kara tsawon wa'adin safarar koko zuwa kasashen ketare


Alassane Ouattara, wanda aka hakikanta shine ya lashe zaben Ivory Coast.
Alassane Ouattara, wanda aka hakikanta shine ya lashe zaben Ivory Coast.

Mutumin da duniya ta amince da shi a zaman wanda ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi a watan Nuwamba a kasar IC, Alassane Ouattara, ya kara tsawon wa’adin haramta safarar Cocoa zuwa kasashen waje

Mutumin da duniya ta amince da shi a zaman wanda ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi a watan Nuwamba a kasar Ivory Coast, Alassane Ouattara, ya kara tsawon wa’adin haramta safarar Cocoa zuwa kasashen waje har zuwa karshen wannan watan. Mr. Ouattara yana kiki-kakar mulki da Laurent Gbagbo, wanda ya ki sauka daga kan kujerar shugabancin kasar. Mr. Ouattara ya haramta fitar da Cocoa zuwa kasashen waje a watan Janairu, bisa fatar toshe kafar da Mr. Gbagbo yake samun kudaden shiga. Wa’adin haramcin na farko zai kare a wannan makon. A halin da ake ciki, fadan da ake gwabzawa a tsakanin magoya bayan shugabannin biyu ya kara matsawa cikin wata unguwar da ake kira Yopougon a birnin Abidjan, inda akasarin mazaunanta masu goyon bayan Mr. Gbagbo ne. A da, akasarin tashe-tashen hankualn da suka biyo bayan zabe a birnin Abidjan su na wakana ne a unguwannin magoya bayan Ouattara. Kungiyar tarrayar Afrika da Majalisar Dinkin Duniya da akasarin kasashen duniya su na goyon bayan Mr. Ouattara a zaman wanda ya lashe zaben shugaban kasar. Mr. Gbagbo kuwa ya dage a kan cewa shi ne ya lashe wannan zabe. Wani babban mashawarcin Gbagbo yace ba su yarda da shawarar da Kungiyar Tarayyar Afrika ta yanke ta amincewa da Ouattara a zaman shugaba ba.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG