Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka da Masar na tattaunawa game da Sinai


John Kerry, Sakataren Harkokin Wajen Amurka
John Kerry, Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya fara tattaunawar difilomasiyya a yau Lahadi da takwaransa Sameh Soukri game da hare-haren ta’addanci a yankin Sinai dake Masar.

Jami’an Amurka sun bayyana cewa Kerry ya zanta da Ministan harkokin wajen Masar din game da damuwar Amurka akan ‘yancin bil’adama a game da hambararren shugaba Mohammed Morsi.

Rabon bangarorin gwamnatin biyu na Amurka da Masar da irin wannan ganawar ido da ido tun a shekarar 2009. Wannan ziyara ce ta kasashe 5 da Kerry ya faro ta Masar.

Masu tsokaci sun ce Mista Kerry na cikin tsaka mai wuyar kamo bakin zaren taya Masar yaki da ‘yan ta’addar ISIS da kuma na kalubalantar siyasar kasar game da take ‘yancin bi’adama.

Musamman ‘yancin ‘yan adawa da kuma na ‘yan jaridu. Inji fitaccen mai sharhin a Amurkan nan akan ci gaban Gabas ta Tsakiya Michele Dunne.

XS
SM
MD
LG