Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Umarci Amurkawan dake Kasar Burundi Su Fice


Sakataren Harkokin Wajen Amurka, John Kerry
Sakataren Harkokin Wajen Amurka, John Kerry

Biyo bayan rikicin da ya barke a Burundi da ya haddasa rasa rayuka fiye da tamanin, ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta umarci amurkawa dake zaune a kasar Burundin da su fice

Gwamnatin Amurka, ta umarci duk ‘yan kasar da ke zaune a Burundi da su fice daga kasar, bayan mummunan fadan da ya barke a makon da ya gabata da ya hada da sojoji da ‘yan sanda.

A jiya Lahadin, ma’aikatar harkokin wajen Amurka, ta ce ta ba da umarnin a kwashe wasu daga cikin ma’aikatanta tare da iyalansu, yayin da rikicin siyasar kasar ta Burundi ke kara ta’azzara bayan zabukan da aka yi da yunkurin juyin mulki a watan Mayun da ya gabata.

Ma’aikatar harkokin wajen ta Amurka, ta kuma yi gargadin cewa ofishin jakadancin Amurkan, zai iya ba da takaitaccen taimako ne kawai a kasar ta Burundi ga Amurkawa.

Akalla mutane 80 aka kashe a ranar Juma’ar da ta gabata a Bujumbura, babban birnin kasar, bayan da wasu mahara suka kai samame a wani sansanin soji, inda aka samu hasarar rayuka, ciki har da jami’an tsaro takwas da kuma wasu daga cikin maharan da dama, kamar yadda wani kakakin soji ya bayyana.

XS
SM
MD
LG