Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AMURKA: Zata Kakabawa China Takunkumi Saboda Leken Asiri


Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Kerry
Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Kerry

Wani rahoto da Jaridar Washington Post ta fitar a daren jiya Lahadi na nunin cewa Amurka na shirin mai da martani ga China kan leken asiri

China na kelen assiran Amurka ta hanyoyin yanar gizo, abinda ya janyo satar bayanan ma’aikatan gwamnatin Amurka, inda zata saka takunkumi kan mutane ko kamfunnan da suka amfana da bayanan sirrin da aka sata.

Jaridar ta Ambato wasu kusoshin gwamnatin Amurka da ba’a bayyana sunayensu sa ban a cewa, har yanzu Amurka bata yanke shawara ba ko zata saka takunkumi ba, amma nan bada dadewa zata yanke shawara kan batun.

Tun ran Daya ga watan Afrilu ne shugaba Obama ya rattaba hannu kan wata doka ta ta umurci baitulmalin Amurka hade da opishin atone-janar na kasar da sakataren harkokin waje, cewa su dakatar da kudade da kaddarorin duk wanda aka samu da laifin leken assiran gwamnatin Amurka da satar bayanai ko cin moriyar su.

An jima ana zargin Kasar China da laifin koarin neman satar assiran kamfanonin Amurka da ma gwamnati. A watan Mayu Amurka ta zargi wasu manyan jami’an Sojoji da satar bayanan kasuwanci kan wasu kamfanonin Amurka. Amma China ta karyata zargin.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG