Mataimakin shugaban kasar ta Najeriya Farfasa Yemi Osinbajo shi ya sanya hannu a madadin Najeriya yayin da daraktan hukumar raya kasashe masu tasowa ko USAID resshen Najeriya Michelle Harvey ya sa hannu a madadin gwamnatin Amurka.
Shirin zai lashe sama da dalar Amurka miliyan biyu ya biyo bayan alkawarin da Amurka ta yiwa Najeriya yayin ziyarar da shugaba Buhari ya kai Amurka a watan Yuli.
Shirin nada zummar marawa Najeriya ta rage matsanancin talauci mai radadi cikin yanayin tsarin dimokradiya wanda zai karfafa tayar da komadar tattalin arziki. Taimakon zai samarda al'umma mai cike da koshin lafiya da kuma karfafa kyakyawan shugabanci na gari.
Ga rahoton Hassan Maina Kaina.