An haura da bakin hauren zuwa gabar jiragen ruwa dake Sisili. Mafi yawancin mutanen daga kasashen Sudan, Eritria da Syria suka fito. Akwai mata da yara da dama a cikin tawagar tsallakewar kamar yadda aka gansu sun yi sahu suna karbar abin sawa a baka.
Wasu kuma bayan an cece su an mika su zuwa garin Pozalo dake kudu maso gabashin Sicily. Ceton ya zo ne kwanaki kadan da kifewar kwale-kwalen wasu bakin hauren da suka nutse a kusa da gabar tekun Libya.
Wadanda suka halaka din a baya duk sun fito ne da Senegal, Mali da Benin kamar yadda hukumar ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya suka sanar.