Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An dau matakan tsaro a jami'o'in Nijeriya bayan wata barazanar Boko Haram


Movement For Democratic Change (MDC) supporters chant the partys slogan as MDC President Morgan Tsvangirai addresses thousands of party supporters at his last campaign rally before elections set for July 31, in Harare.
Movement For Democratic Change (MDC) supporters chant the partys slogan as MDC President Morgan Tsvangirai addresses thousands of party supporters at his last campaign rally before elections set for July 31, in Harare.

‘Yan sandan Nijeriya sun karfafa matakan tsaro a wasu

‘Yan sandan Nijeriya sun karfafa matakan tsaro a wasu jami’o’i bayan da su ka sami barazana daga tsattsaurar kungiyar Islamar nan da ta kai wasu munanan hare-hare cikin ‘yan watannin nan.

Hukumomi sun ce kungiyar Boko Haram, wadda sunanta ya samo asali daga akidar cewa “tsarin ilimin yammacin duniya haramun ne,” ta yi barazanar kai hare-hare kan wasu jami’o’i a fadin Nijeriya.

An tsaurara matakan tsaro a harabobin Jami’o’in Ibadan da Benin, wadanda dukkanninsu ke kudancin Nijeriya.

Yakan yi wuya a tantance barazanar Boko Haram saboda yadda shugabancinta da kuma mai magana da yawunta fiye da daya.

A jiya Talata, wata kotu a Nijeriya ta tuhumi wasu mutane 8 da ake ganin ‘yan Boko Haram ne da hannu a jerin hare-haren bama-bamai da harbe-harbe a sassan babban birnin kasar tsakanin watan Maris da Yuli wadanda su ka yi sanadin mutuwar mutane 25.

Kungiyar ta Boko Haram tad au alhakin harin bam din da aka kai a hedikwatan Majalisar Dinkin Duniya da ke Abuja a watan jiya da kuma wanda aka kai a harabar hedikwatar ‘yan sanda a watan Yuni.

XS
SM
MD
LG