Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An fara babban zabe na kasa a Najeriya


Voters queue to register during parliamentary elections in Kano, northern Nigeria.
Voters queue to register during parliamentary elections in Kano, northern Nigeria.

Yau ake gudanar da zaben sabuwar majalisar tarayya a Najeriya

Yau ake gudanar da zaben sabuwar majalisar tarayya a Najeriya, wanda ya kasance zaben farko a jerin zabukan da za a dauki makonni uku ana gudanarwa. Masu sa ido suna jira su ga ko jami’an zabe zasu iya hana aukuwar tashin hankali da kuma kazamin magudin da aka tafka a zabukan da aka gudanar cikin shekara ta dubu biyu da bakwai, wanda masu sa ido na Kungiyar Tarayyar Turai suka bayyana a matsayin marar inganci, aka kuma dauki watanni ana kalubalantar zaben a kotuna. Shugaban hukumar zabe Attahiru Jega ya bayyana jiya jumma’a cewa, zaben da za a gudanar a wannan watan na Afrilu, wata dama ce da ‘yan Najeriya suke da ita na gyara kura-kuran da aka yi a lokutan baya. Babban magatakardar Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-Moon ya bayyana gamsuwa da ci gaban da aka samu a Najeriya, ya kuma yi fatar zaben zai zama karbabbe ga ‘yan Najeriya da kuma al’ummar kasa da kasa. An yi fama da tashe tashen hankali a Najeriya yayinda ake shirin gudanar da zabukan musamman a arewacin kasar. Babu tabbacin ko dukan tashe tashen hankalun suna da nasaba da siyasa. An rufe kan iyakokin kasar da tafi kowacce yawan al’umma a Afrika daga karfe sha biyun rana jiya jumma’a zuwa shida na safiyar Lahadi. Hukumomi zasu kuma kayyade shawagin ababan hawa yayinda jama’a suke kada kuri’a.

XS
SM
MD
LG