Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Hallaka Mutane A Hare-Haren Bam Da Daren Jiya A Jos


Sufeto-Janar na 'yansandan Najeriya Solomom Arase
Sufeto-Janar na 'yansandan Najeriya Solomom Arase

Bayan wani dan lokaci na kwanciyar hankali a Jos, babban birnin jahar Filato, jiya da dare an kai wasu hare-haren bam biyu, wadanda su ka hallaka mutane.

Wasu da har yanzu ba a tantance ko su waye ba, sun hallaka mutane da hare-haren bama-bamai da daren jiya a Jos, babban birnin jahar Filato.

Wakiliyarmu a Jos Zainab Babaji ta shaida ma abokin aikinmu Ladan Ibrahim Ayawa cewa bam na daya ya tashi ne da misalin karfe tare na dare a wani wurin cin abinci da ake ma lakabi da Sha Shagalika, mallakin wata mata mai suna Hajiya Talatu, a Bauchi Road – wato kusa da tashar motar zuwa Bauchi.

Zainab ta ce wadanda ta zanta da su sun ce sun ga gawarwaki a ciki da wajen shagon. Ta ce saboda kowa ta kansa yak e yi bayan harin, wadanda ta zanta da su sun ce bas u iya kirga gawarwakin ba a wurin cin abincin.

Ta ce bam na biyun kuma ya tashi ne ‘yan dakikoki kadan bayan na Bauchi Road din. Kuma ya tashi ne a ‘Yan Taya daura da inda Sheikh Sani Yahaya Jingir ke gabatar da tafsirin watan Ramadan. Zainab ta ce wanda ya mana bayani y ace maharin ya je wurin ne da farin kaya ya harba bam, sai kawai aka ji bam kuma ya tashi. To saidai ta ce wanda ya ma ta bayani y ace bai ga gawa da idanso ba a lokacin kodayake dare ne don haka ta yiwu akwai gawa ko gawarwaki . Ta ce ta yi ta kiran jami’an tsaron don jin abin da su ka sani da kuma matakan da su ke daukawa amma ba su dauki waya ba.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:03 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG