Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Ja Kunnen 'Yan Kungiyar MEND


Shugaban wata kungiyar matasan Arewa yace idan har 'yan yankin Niger Delta suka naiwatar da barazanarsu, to zasu tsokano abinda ba su san iyakarsa ba

Shugaban wata kungiya ta matasan arewacin Najeriya, ya gargadi 'ya'yan kungiyar tsdageran yankin Niger Delta, MEND, da cewa idan suka kuskura suka aiwatar da barazanarsu ta kai farmaki a kan Musulmi, su na iya tsokano abinda ba zasu iya magance shi ba.

A cikin hirar da yayi da Muryar Amurka, malam Aminu Aliyu Kofar Sauri, yace babu wata hujja da 'yan kungiyar ta MEND suke da ita, ta kai farmaki a kan dukkan al'ummar Musulmi dangane da hare-haren da ba a ma tabbatar da ko su wanene suke aikata su a Najeriya da sunan Boko Haram ba.

Ya ce idan har matasan na yankin Niger Delta su na jin cewa su na da matasa 'yan ga-ni-kashe-ni, a arewa ma akwai irin wadannan matasa n, wasu ma wadanda ba a san su ba, balle ma a ce za a ja musu kunne kan kada su maida martani.

A saurari matakai guda uku na gargadin da shugaban matasan na arewa yayi ma 'yan MEND na Niger Delta:
Martani Ga 'Yan MEND Daga Aminu Aliyu Kofar Sauri Katsina - 2:07
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:07 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG