WASHINGTON, DC —
Shugaban wata kungiya ta matasan arewacin Najeriya, ya gargadi 'ya'yan kungiyar tsdageran yankin Niger Delta, MEND, da cewa idan suka kuskura suka aiwatar da barazanarsu ta kai farmaki a kan Musulmi, su na iya tsokano abinda ba zasu iya magance shi ba.
A cikin hirar da yayi da Muryar Amurka, malam Aminu Aliyu Kofar Sauri, yace babu wata hujja da 'yan kungiyar ta MEND suke da ita, ta kai farmaki a kan dukkan al'ummar Musulmi dangane da hare-haren da ba a ma tabbatar da ko su wanene suke aikata su a Najeriya da sunan Boko Haram ba.
Ya ce idan har matasan na yankin Niger Delta su na jin cewa su na da matasa 'yan ga-ni-kashe-ni, a arewa ma akwai irin wadannan matasa n, wasu ma wadanda ba a san su ba, balle ma a ce za a ja musu kunne kan kada su maida martani.
A saurari matakai guda uku na gargadin da shugaban matasan na arewa yayi ma 'yan MEND na Niger Delta:
A cikin hirar da yayi da Muryar Amurka, malam Aminu Aliyu Kofar Sauri, yace babu wata hujja da 'yan kungiyar ta MEND suke da ita, ta kai farmaki a kan dukkan al'ummar Musulmi dangane da hare-haren da ba a ma tabbatar da ko su wanene suke aikata su a Najeriya da sunan Boko Haram ba.
Ya ce idan har matasan na yankin Niger Delta su na jin cewa su na da matasa 'yan ga-ni-kashe-ni, a arewa ma akwai irin wadannan matasa n, wasu ma wadanda ba a san su ba, balle ma a ce za a ja musu kunne kan kada su maida martani.
A saurari matakai guda uku na gargadin da shugaban matasan na arewa yayi ma 'yan MEND na Niger Delta: