Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kafa Dokar Hana Fita A Bauchi


Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda
Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda

An kafa dokar hana fita a Bauchi bayan da wasu 'yan bindiga da ake zargin 'yan Boko Haram ne suka kai hari a wasu sassan jihar.

Rahotanni daga jihar Bauchin Najeriya na cewa an saka dokar hana fita a wasu sassan jihar yayin da sojoji ke fafatawa da mayakan Boko Haram.

Hukumomin jihar sun ce an saka dokar ne saboda a kare rayuka da dukiyoyin mutane.

Wannan saka doka na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ke zargin cewa an saka dokar ne saboda a yi magudin zabe, saboda gwamnati mai ci ta ga 'yan adawa na samun nasaara.

Sai dai gwamnatin kasar ta musanta wannan zargi inda su ka jaddada cewa kare rayuka ake so a yi.

A jiya ne ‘yan kungiyar ta Boko Haram su ka kai hari a jihar Gombe da ke makwabtaka da Bauchin lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama yayin da ake gudanar da zabuka.

Hukumar zaben kasar ta tsawaita wa’adin kammala zaben a wasu sassan kasar zuwa yau lahadi bayan da aka fuskanci wasu matsaloli da suka shafi tsaro da jinkirin zuwan kayayyakin zabe.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:49 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG