Mutane akalla 48, cikinsu harda yara kanana 11, aka kashe a cikin wani mummunan fadan da ya kaure tsakanin wasu kabilu biyu na lardin Tana dake gabashin kasar Kenya.
A yau ne ‘yan sandan kasar suke fadar cewa duk wadanan mutanen da aka kashen, ko dai an sare su ne ko kuma an kona su kurumus, a lokacin da wannan artabun ya gwabce tsakanin kabilun Pokomo da na Orma, wadanda sun yi shekaru suna irin wannan rigimar a kan batun mallakar feguna da tafkunansu na ruwa.
A yau ne ‘yan sandan kasar suke fadar cewa duk wadanan mutanen da aka kashen, ko dai an sare su ne ko kuma an kona su kurumus, a lokacin da wannan artabun ya gwabce tsakanin kabilun Pokomo da na Orma, wadanda sun yi shekaru suna irin wannan rigimar a kan batun mallakar feguna da tafkunansu na ruwa.