Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kai Hari Kan Kakakin Majalisar Taraba


Gwamnan Jihar Taraba, Danbaba Suntai
Gwamnan Jihar Taraba, Danbaba Suntai

Kakakin majlisar dokokin jihar Taraba ya tsallake rijiya da baya sanadiyar wani hari da aka kai masa.

An kai ma kakakin majalisar dokokin jihar Taraba Mr. Haruna Tsokwa hari a kauyen Bade dake jihar Kaduna tsakanin Jos da Abuja.

Harin ya zo kwana biyu bayan da kakakin ya shaidawa kotun da gwamna Danbaba Suntai ya shigar da kara cewa wasikar da aka ce gwamnan ya rubuta wa majalisar na cewa ya dawo daga jinya wasika ce ta bogi.

Maharan sun kai harin ne yayin da yake kan hanyarsa daga Abuja zuwa Jos. Kakakin na dawowa ne daga taron 'yan majalisun jihohi da suka yi a Obudu jihar Cross Rivers. Kodayake Mr. Haruna Tsokwa ya tsallake rijiya da baya to amma an harbi daya daga cikin 'yansandan dake tare da shi. Hadimin kakakin ta fuskar yada labarai Tanko Kaura ya ce kakakin na cikin koshin lafiya yayin da aka kwantar da dansandan a asibiti.

Tun dawowar gwamna Danbaba Suntai jihar Taraba ta samu kanta a wani dambarwar siyasa. To sai dai mukaddashin gwamnan Alhaji Garba Umar ya cigaba da kiran 'yan jihar su sani cewa shi ba wata gwamnati daban ya ke yi ba. Yana cigaba ne da aikin mai gidansa gwamna Suntai. Don haka a yi masa fatan alheri domin jihar ta cigaba.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:29 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG