Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kara Tsayin Dokar Ta Baci A Turkiyya


Shugaban Turkiya Racep Tayyib Erdogan ya fadada dokar ta baci a hukumance da aka kafa bayan wani juyin mulki a shekarar 2016 da bai yi nasara ba, yana cewar za a ci gaba da wannan dokar har sai kasar ta samu cikakken kwanciyar hankali da zaman lafiya.

Erdogan ya bayyana haka ne a jiya Lahadi a birnin Ankara gaban dubban mabiyansa da yan jami’iyarsu ta Justice and Development Party da suka kira da a sake zaben dayan uban jami’iyasu ya ci gaba da rike mukamin.


Wannan dokar ta bacin, ta na baiwa Erdogan da hukumar zantarwarsa damar kafa dokoki ba tare da umarnin majalisa ba ko shawarar sashen shari’a.


Sanarwa Erdogan da kuma sake dawowa ya nemi mukamin shugaban jami’iya ya zo ne bayan mako hudu da Turkiya ta gudanar da wata kuri’ar raba gardama a kan fadada ikon shugaban wanda ya yi karamin nasara a kuri’ar.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG