Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Masar-An Kashe Mutane 13 Sakamakon Arangama Tsakanin 'Yansanda da 'Yan Muslim Brotherhood


Masu zanga zanga suke gudu daga borkonon tsohuwa da 'Yansanda suka harba
Masu zanga zanga suke gudu daga borkonon tsohuwa da 'Yansanda suka harba
A Misra kuma hukumomin kasar sun bada labarin cewa an kashe mutane 13 a duk fadin kasar jiya jumma’a, lokacinda ‘yansanda suka yi kokarin tarwatsa zanga zangar da dubban magoya bayan kungiyar ikhwanul Muslimin ko Muslim Brotherhood da turanci suka shirya, na neman ganin an maido da shugaban kasar Mohammed Morsi da sojoji suka hambaras kan iko.

Shadiun sun ce ‘Yansanda basu yi wata wata ba wajen tarwatsa zanga zangar da aka shirya a Alkahira, da Ismaliya, da Alexandria da kuma Giza. Tunda farko hukumomin kasar sun yi kashedin cewa basu amince da duk wata zanga zanga daga ‘yan kungiyar ba, bayanda masu iko a kasar suka ayyana kungiyar a matsayin ta ‘yan ta’adda cikin watan jiya.

Ma’aikatar kiwon lafiya kasar tace biyar daga cikin wadanda rikicin ya rutsa da su sun gamu da ajalinsu ne a birnin Alkahira, sai dai ma’aikatar batayi bayani ko wadnasda aka skashen ‘Yansanda ne ko masu zanga zanga ko kuma ‘yan kallo ne.

Gwamnatin kasar wacce take samun goyon bayan sojoji, da suka kifar da gwamnatin Mr. Morsi cikin watan Yulin bara, suna amfani da ayyana kungiyar ta Muslim Brotherhood a matsayin ta “Yan ta’adda” wajen tsare daruruwan magoya bayan kungiyar. Wasu dubbai ciki harda shugabannin kungfiyar ana daure dasu na wattani.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG