Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kashe Mutane 38 A Wata Tarzoma A Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya


Mutane 38 aka hallaka, aka raunana wasu fiyeda 50 a cikin wata mummunar tarzomar da ta barke ranar Larabar shekaranjiya a Junhuriyar Afrika ta Tsakiya.

Ance tashin hankalin ya samo asali ne daga lokacinda mayakan ‘yantawayen Seleka suka abkawa garin Kanga-Bandoro inda sojan kiyaye sulhu na M-D-D suka tinkare su, har suka kashe 12 daga cikin ‘yantawayen.

Sai dai kuma cikin wadanda suka rasa rayukkan nasu akwai harda fararen hula 9.

Ana jin wannan farmakin kamar ramuwar gayya ce su mayakan Seleka din suka kai don rama kisan gillar da aka yi wa wani dan’uwansu, a cewar rundunar kiyaye sulhun MDD din.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG