Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kashe Sama Da Mutane Hamsin A Wata Zanga Zanga


Sama da mutane hamsin aka kashe a jihar Oromiya ta kasar Ethiopia a loakcin da yan sanda suka sake hayaki mai sa hawaye da harbin gardi don tarwatsa masu zanga zangar kin jinin gwamnati a wurin wani bukin addini.

Hayakin mai sa hawayaen ya yi sanaidiyar turmutsutsu a jiya Lahadi. Jami’ai a kasar sun bada sanarawar cewa mutane 52 ne aka kashe.

Gwamnati tace mutane da dama ne suka jikata a wannan tarzomar da ta tashi a wurin bukin shekara inda kabilar Oromo ke shagalin kawo karshen damana.

Dubban mutane ne suka taru a gabar kogin Harsadi don yi bukin godiya ta shekara a garin Bishoftu mai tazarar kilomita 40 daga babban birnin kasar Addis Ababa.

An taba samun makamanciyar wannan gagarumar zanga zanga a Oromiya shekaru biyu da suka wuce, da farko takaddama a kan fili ne ya janoyta.

Mutane da yawa sun sha rasa rayukkansu a irin wadanan tashe-tashen hakullan a kasar ta Ethiopia daga shekarar 2015 zuwa yanzu.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG