Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Buhari Yayi Nasara


Dan takarar shugabancin kasa kuma tsohon shugaba Muhammadu Buhari kafin ya gabatar da kudurinsa a taron fidda gwani da APC tayi, Disamba 11, 2014.
Dan takarar shugabancin kasa kuma tsohon shugaba Muhammadu Buhari kafin ya gabatar da kudurinsa a taron fidda gwani da APC tayi, Disamba 11, 2014.

Tsohon Shugaban Kasa Janar Muhammadu Buhari ne yayi nasarar lashe zaben fidda gwani na takarar shugabancin Najeriya a karkashin jam'iyyar APC mai adawa.

A filin wasa na Teslim Balogun dake birnin Ikko a Najeriya, aka kirga kuri’un zaben fidda gwani na dan takarar shugabancin kasa a karkashin jam’iyyar APC mai adawa.

An kirga kuri’un kowani dan takara ne a lokaci daya, kafin a kammala tantance jimlar kuri’un da kowani dan takara ya samu.

‘Yan takarar sune tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, gwamnan Jihar Kano Rabiu Musa Kwankwaso, gwamnan Imo Rochas Okorocha, tsohon shugaban kasa Janar Muhammadu Buhari da shugaban kamfanin jaridar Leadership Sam Nda Isaah.

Ga yadda sakamakon yake a halin yanzu, daga wakilin Muryar Amurka, Hassan Umaru Tambuwal.

Atiku Abubakar - 954

Muhammadu Buhari - 3430

Rabi'u Musa Kwankwaso - 974

Rochas Okorocha - 624

Sam Nda Isaah - 10

Jam'iyyar PDP mai mulki a Najeriya ta kammala zaben fidda gwaninta, inda shugaba mai mulki Goodluck Jonathan ya karbi akalar takarar, tare da mataimakinshi Namadi Sambo.

Jaddawalin Sakamakon Zaben Fidda Gwani na Tsayawa Takarar Shugaban Kasa a APC, daga wakilin Muryar Amurka Hassan Umaru Tambuwal.

Dan Takara

Adadin Kuri’u

Atiku Abubakar

954

Muhammadu Buhari

3430

Rabiu Musa Kwankwaso

974

Rochas Okorocha

624

Sam Nda Isaah

10

XS
SM
MD
LG