Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sace ‘Yan Sandan Kasa da Kasa


Rundunar kare zaman lafiya ta hadin gwiwar MDD da Tarayyar Afirka, UNMID, ta bada sanarwar sace jami’an ‘yan sandanta biyu ran Asabar da safe a Nyala, cibiyar yankin kudancin Darfur-kasar Sudan.

MDD tayi yekuwar cewa an sace jami’anta biyu, masu ayyukan badashawara ga ‘yan sandan kasa da kasa dake aiki a rundunar hadin gwiwar kare zaman lafiya ta MDD da tarayyar Afirka dake yankin Darfur.

Rundunar hadin gwiwa ta ayyukan kare zaman lafiya, UNMID, tace a ran Asabar da safe ne a Nyala, cibiyar yankin kudancin Sudan dake Darfur, wasu katti uku a cikin mota suka kame jami’an na MDD bayan sun fito daga masaukinsu kan hanyarsu ta zuwa sansanin sojin hadin gwiwa, bayan sun yi barazanar harbesu da bindiga sannan suka cusasu a mota suka tsere dasu. MDD tace zata gudanar da cikakken bincike.

XS
SM
MD
LG