Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An sako baturiyar da aka sace watan jiya a tsakiyar Najeriya.


(File Photo)
(File Photo)

An sako baturiyar nan ‘yar shekaru 71 dake aiki mishan da aka sace watan jiya a tsakiyar Najeriya.

An sako baturiyar nan ‘yar shekaru 71 dake aiki mishan da aka sace watan jiya a tsakiyar Najeriya.

Majami’ar Methodist dake nan Amurka tace an mika Phyllis Sortor ga shugabannin darikar.

Bishop David Kendall ya bayyana a wata sanarwa da aka buga a shafin yanar gizo na majami’ar cewa, Sortor ta san aikinta yana da hatsari, sai dai ta kuma sani cewa wurare kalilan ne a duniya da basu da hatsari.”

Sortor da aka sace a harabar makarantar Hope Academy dake Emiwroro jihar Kogi, ta taka rawa gaya wajen kafa makarantu da dama a jihar Kogi domin ilimantar da ‘ya’yan Fulani makiyaya.

Tashar NBC News ta bada rahoto cewa, wadanda suka yi garkuwa da Sortor sun tuntubi aminiyarta suka nemi a biyasu diyyar dala dubu dari uku.

Kungiyar Boko Haram bata kai hare hare a jihar da aka sace ma’aikaciyar mishan din.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kogi ya fada a lokacin da aka sace ta cewa, ya hakikanta, garkuwa da ita da aka yi aikin masu aikata miyagun laifuka ne.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG