Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Zargi Gwamnatin Jihar Rivers Da Taimakawa Wani Alkali Ya Arce Da Kudin Sata


Nigeria Currency
Nigeria Currency

An zargi gwamnatin jiha Rivers da daukar dawainiyar hayar ‘yan daba, domin bayanai sun nuna cewa wani alkali a jihar ta Rivers ya boye kudi har tsabar dalar Amurka miliyan biyu a cikin gidan sa.

Hukumar ‘yan sanda masu sanye da farin kaya wadda it ace takai wani sumame tace an tsere da duka kudaden zuwa wani wuri da a sani ba, tare kuma da taimakon gwamnan jihar Rivers Nyeso Wike din ne aka yi hakan.

Hukumar tace tana aiki tukuru domin ganin ta gano inda aka kai wadannan kudaden, yanzu haka rundunar ‘yan sandar farin kayan tace tana kokarin ganin ta gurfanar da wadannan alkalan da aka kama.

Wakilin sashen Hausa Lamido Abubakar, yayi kokarin ji daga bakin gwamnatin jihar ta Rivers kome yasa ta sa baki cikin wannan batu hakan bai cimma nasara ba.

Ga dai Lamido Abubakar din da Karin bayani 3’45

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:45 0:00

XS
SM
MD
LG