Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu Shugabannin Afirka Sun Yi Taron Koli Kan Rikicin kwango Sai Dai...


Mutane suke tserewa daga birnin Goma lokacinda fada ya barke tsakanin 'yan tawaye da sojoin gwamnati.
Mutane suke tserewa daga birnin Goma lokacinda fada ya barke tsakanin 'yan tawaye da sojoin gwamnati.
Asabar wasu shugabnnin Afirka sun yi taro da nufin warware rikicin ‘yan tawayen a jamhuriyar demokuradiyyar kwango, suka yi kira ga ‘yan tawayen su “dakatar da duk wata harkar yaki”, kuma su janye daga birnin Goma mai muhimanci da suka kama a farkon makonnan.

Sanarwar da shugabannin suka bayar a jiyan, ta kuma yi kira ga ‘yan tawayen su bar zancen kifar da gwamnatin kwangon.

Shugabannin kasashen Uganda, da Kenya, da Tanzania, da kuma na jamhuriyar Demokuradiyyar kwango ne suka gana a Kampala babban birnin Uganda, amma takwaranso daya wanda yake da muhimmanci da bai sami halarta ba shine shugaban Rwanda paul Kagame, wanda ya soke zuwa a kurarren lokaci, ya tura ministan harkokin wajen kasar a madadin kansa.

Majalisar Dinkin Duniya ta zargi Rwanda cewa tana goyon bayan kungiyar ‘yan tawaye da ake kira M23 a jamhuriyar ta kwango, zargind huku8momin kasar suka musanta.
'Yan tawayen Kwango a garin Sake a lokacinda suke sintiri.
'Yan tawayen Kwango a garin Sake a lokacinda suke sintiri.

Taron kolin da shugabannin suka yi a kampala yazo ne a dai dai lokacind aake nuna damuwa kan dannawar da ‘yan tawayen suke yi zuwa gabasghin kwango, da kuma canji da aka samu a rundunar mayakan kasar.

Shugaban kasar Kwango Joseph Kabila ya dakatar da babban hafsan hafsoshin kasar Janar Gabriel Amisi kan zargin yana sayarwa ‘yan tawaye a gabashin kasar makamai.
Dakatarwar da aka yi wa janar Amisi tazo ne kwanaki uku bayan da dakarun ‘yan tawaye suka sami nasara kan sojojin kwango suka kama birnin Goma.
XS
SM
MD
LG