Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An yi Zaben Kananan Hukumomi a Jahar Yobe


Jami'an hukumar zaben Najeriya.
Jami'an hukumar zaben Najeriya.

Sai dai an yi zaben kananan hukumomin ba tare da PDP ba wadda ita ce babbar jam'iyar hamayya a jahar Yobe

Kamar yadda gwamnatin jahar Yobe ta dage cewa sai an yi zabe, ba gudu, ba ja da baya, karshen ta dai an yi zaben kananan hukumomi a jahar asabar din nan, sai dai ba a samu cikowar masu kada kuri'a ba kamar yadda aka saba . Wannan ne karo na farko acikin shekaru biyar da aka yi zaben kananan hukumomi ba tare da jam'iyar PDP ba, wadda ita ce babbar jam'iyar hamayya a jahar Yobe. Kuma wannan ne karo na biyu da jam'iyar ta PDP ke kauracewa zabe a jahar Yobe. Wakilin Sashen Hausa Haruna Dauda Biu ya aiko da rahoto daga Damaturu babban birnin jahar Yobe:

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:37 0:00
Shiga Kai Tsaye

Haruna Dauda Biu ya kara cewa al'amura sun tsaya cak a jahar ta Yobe sakamakon takaita zirga-zirgar ababen hawa domin a gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG