Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yi Zanga Zanga a Jahar Rivers


An yi zanga-zangar rashin yarda da jinkirta zabe, Fabrairu 5, 2015.
An yi zanga-zangar rashin yarda da jinkirta zabe, Fabrairu 5, 2015.

Rahotanni daag Jihar River da ke Kudu maso kudancin Najeriya na cewa, har yanzu wasu kungiyoyi fararen hula, na ci gaba da gudanar da zanga zanga domin neman a soke zaben jahar da aka gudanar a kwanan nan.

Wakilin Muryar Amurka Sanusi Lamido ya kara da cewa ko a baya bayan nan an samu kungigoyin kasa da kasa da suka gudanar da taruka na neman a soke zaben domin irin magudin da suka ce an tafka.

Sun kuma yi zargin cewa an tursasa mutane wajen yin zabe kana an razana wasu da dama ta hanyar harbe-harben bindiga a lokacin zaben.

Zaben na Jahar Rivers ana takaddama ne tsakanin dan takarar PDP Nyesom Wike da Dakuku Peterside na jam’iyar adawa ta APC.

A baya bayan nan ‘yan jam’iyyar ta APC suka gudanar da zanga zanga a ranar juma’ar da ta gabata a gaban ofishin hukumar zabe ta INEC bayan da hukumar zaben ta yi jinkiran bin umarnin kotu.

A kwanan ne kotun sauraren korafe-korafen zabe ta nemi hukumar at INEC da ta mika mata takardunzaben jihar.

A daya bangaren kuma, hukumar ta INEC ta ayyana cewa a ranar 23 na wannan wata za a gudanar da zaben kananan hukumomi a jahar.

Ga karin bayani daga wakilinmu Sanusi Lamido a tattaunawarsu da Halima Djimrou:

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG