Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yima Ministan Ilimin Najeriya Bore a Jihar Gombe


Ministan Ilimin Najeriya Ibrahim Shekarau.
Ministan Ilimin Najeriya Ibrahim Shekarau.

Da isar Ministan Ilimin Najeriya Jihar Gombe anyi zanga zangar Lumana

Daliban kwalegin horas da malamai ta garin Gombe sunyi wani zanga zangar lumana, a lokacin da Ministan Ilimin kasar Mal. Ibrahim Shekarau, ya kai wata ziyara a kwalegin. A jawabinshi yayi maganar cewar wannan ziyarar da sukeyi duk sati suna duba aiyukan da gwamnati tarayya taba ma ‘yan kwangila ne, ko suna yi yadda yakamata, da kuma tattaunawa da hukumomin makarantun don jin matsalolinsu, kana da daliba.

Amma dai a cikin bayanin nashi bai tabo maganar zanga zangar daliban ba. Su dai daliban sun nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnati ke nuna halin ko inkula a fannin ilimi. Inda suke cewar basu da ruwansha balle ma na wanka. Mafi akasarinsu suna amfani da ruwan leda ne su yi wanka ko wani bukatunsu. Sun kuma ce babu kayan karatu da dai sauran abubuwan da yakamata ace dalibai na moremawa.

An Yima Ministan Ilimin Najeriya Bore a Jihar Gombe - 2'10"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:10 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG